HUDAH 126~130
[05/06, 7:47 PM] Feedoh✍🏻✍🏻: ⭐⭐HUDAH⭐⭐
Na
Feedoh & Meesha Lurv
1⃣2⃣6⃣~1⃣3⃣0⃣
Haka rayuwa tadinga wakana tsakanin naufal da huda, cikin so da k'aunar juna,"kowa burinshi yafarantama d'ayanshi rai,"satin hudah ukku gidan naufal wani irin kyau tayi tayi k'iba b'ulb'ul abinta, duk wanda yaga hudah saita bashi sha'awa,"HUDAH ce kwance bisa cinyar naufal tanamai shagwab'a shiko saifaman washe baki yake kamar gonar audiga lolzzx, cikinta ya shafa yace princess Anya banyi ajiyaba zaro ido tayi tace ba wata ajiya dariya naufal yayi yace matsoraciya, dariya hudah tayi tace naji dai"naufal yace princess ki shirya anjima zamuje gidan maaah da gidansu mammy saboda gobe nakesan mukoma kd,"rungumoshi tayi tace datz my hubby, I Lurv u so much, murmushi yayi yace Lurv u more my baby doll..
******************
"Hudah yace tsaye, tana cewa AD nafa shirya tun d'azu amma katsayaman yanga, "murmushin k'eta yayi yace yarinya nafasa zuwa kuma,"rungumoshi tayi ta baya ta d'aura kanta bisa bayanshi, tace haba mijina dan Allah kayi hak'uri Allah nasaka raina, rungumota naufal yayi yace wasa nakemaki princess yanzu zamu tafi, kiss ta mannamashi tace tnx my baby, murmushi yayi.saida naufal yagama ja mata rai kana ya shirya sukatafi, fira yake janta dashi a hanya amma hankalinta yatafi wajen taje tagama d'inta dan gaskia tayi mssn enta saidai waya da sukeyi kullum.
Tun naufal bai ida tsayawaba Hudah ta b'alle marfin mota tafita da gudu, dariya naufal yayi yace naga randa hudah zata girma, "tundaga zaure take kwalama maaah kira, sallah maaah keyi, hudah nashigowa maaah na daidai sallamewa fad'awatayi kan maaaah tana dariya tace maaah d'ina nayi mssn enki, dariya maaah tayi tace aygara ki karyani, suna cikin haka yara suka dinga shigowa da kayan abinci ita kanta hudah batasan dasuba "maaah tace autah kedawa wai kikazo ne? Hudah tace nida ya naufal, maaah tace kuma kika barshi waje?,bata kaigaba maaah ansaba sukaji sallamar naufal,"wuri yasamu kusada hudah yazauna ya gaishe da maaah cikin girmamawa, "maaah ta amsa tana murmushi, juyowa yayi wajen hudah yace kardai ki karyaman mama, dariya maaah tayi tace kaima madai fad'a, tazo zata k'arasa yar tsohuwa, dariya duka sukayi,"naufal ne yace maaah dama munzo maku bankwana ne saboda gobe in shaa Allah zamuwuce kaduna, gyada kai maaah tayi tace Allah yakaimu, maaah tayaba da irin rik'on da naufal yama d'iyarta nan tak'arayimasu nasiha dasu zauna lapia, kuma su rik'e juna da amana, "maaah tace kuje kugaida su alhaji, gyad'a kai Hudah tayi kana suka tashi...
K'ofar gida sukaci karo da daddy, duk'awa naufal yayi har k'asa yagaidashi daddy ya amsa yana murmushi,"yace ah wanike gani haka kamar d'iyata duk'ar da kaitayi k'asa tana murmushi tace daddy ina wuni amsawa yayi yace lapia lau hudah nah,"kinsanko gobe nake cewa zanje nagano d'iyata, hudah tace daddy ayni gashi nakasa hak'ura sai gobe nazo naga iyayena, dariya daddy yayi yace ayko kun kyauta, mushiga daga ciki,"tanayin sallama parlour tacikaro da fady wani ihu fady tasaka, saida kunnena yamsa😡, mak'alkale hudah tayi, hudah ta tureta tace ni fushi nake dake," kunne fady takama tace am sowee swt sis wlhi daddy ne yahanani zuwa wai karna takura maki,"dariya hudah tayi tace ina mummy? Fady tace mummy nasama,hannun hudah fady taja sukayi sama d'akin mummy," fady ce ke kwalama mummy Kira, mummy tace wai lapia, dariya fady tayi tace bak'uwa nakawo maki,mummy naganin hudah tafara washe baki amare kune yau,sannu da zuwa d'azu muke magarki da daddynku, hudah har k'asa ta duk'a ta gaida mummy, amsawa mummy tayi cikin kulawa tace ya naufal d'in hudah tace yana tare da daddy, " fira sukayi sosai, "hudah tace wai mummy ya maganan haneef da fady ne? Mummy tace ay daddynku yamashi magana yace abasu nan da sati biyu, hudah tace, Allah yakaimu, suna tsaka da fira saiga daddy ya shigo yace hudah Ashe gone Kaduna kuka nufa? Hudah tace eh daddy dama bankwana mukazo maku, daddy yace Masha Allah, kima naufal godia naga kayan abinci nagode, " kwarai hudah taji dadin abinda naufal yayi tace bakomai daddy mummy ma tayi godia kana suka sakko parlour nan mummy suka gaisa da naufal takuma yimai godia,"nasiha daddy yak'ara yimasu kana suka masu sallama suka koma gidan maaah, nanma sunyi fira kana suka ma maaah sallama suka wuce k'warai maaah taji daban itako hudah hard a kukanta.
Gidansu naufal suka wuce, nanma sunyi fira dannan sukayi dinner ,"papa ne ya had'asu yamasu nasiha, yace naufal kaine namiji kuma hudah amanace hanunka kaji tsoron Allah karik'e huda da amana, "kekuma hudah kibi mijinki sauda k'afa kinjiko, hudah tace in shaa Allah daddy, zaku iya tafiya Allah yamaku albarka yakaiku lapia kuma, suka amsa da amin kana suka tafi wajen mammy, nan madai masihar mammy tamasu, kana taba hudah humra dasu turaruka, "naufal yace ina nawa yake? Mammy tace baka dashi, naufal yace ay maryan papa tabani yayi waje da sauri yana dariya, dariya mammy tayi tace da ka tsaya mana...
www.phirdauceejeebo.mywapblog.com
Written by
Firdausi Abdul'Azeez (Feedoh) &
Ayeesha Musa (Meesha Lurv).
[05/06, 9:29 PM] Feedoh✍🏻✍🏻: ⭐⭐HUDAH⭐⭐
Na
Feedoh & Meesha Lurv
1⃣3⃣1⃣~1⃣3⃣5⃣
Hudah ce kwance cikin bargo tana zazzab'i, AD ne gefenta yace princess anya zan iya tafiya aiki nabarki haka? Da kyar take iya d'aga kanta tace AD kaje kawai, naufal yace kodai mutafi asibiti tunda jikin yayi zafi haka? Kafin tabashi amsa tuni tafara amai kamar hanjinta zasu fita,"saida yabari tagama kana yad'auketa caf yayi toilet da ita, wanka yamata kana yaxo ya shiryata, waya ya d'auka ya kira doctor Maryam Ladan Shuni, yagaya Mata abinda ke damun hudah, d'ayan b'angaren doctor Maryam tace shikenan gani nan zuwa nanda 20mnt,ok naufal yace kana ya aje waya, "yanan zaune wayanshi yayi rngn yana d'agawa ya doctor ce amsa wayan yayi kana yace ta shigo,da sallama doctor Maryam ta shiga d'akin sun gaisa da naufal kana ta yaye blanket d'in da hudah ta rufa, gwaje gwaje naga tayi,can naga ta d'ago tana murmushi, cema naufal tayi congrtz matarka na d'auke da ciki na 8weekz wani tsalle naufal yayi yace Allah na godema, kyauta yama doctor tayi godia ta rubuta mahungunan dazai siyoma hudah, kuma kar abar hudah tayi aikin wahala..
Hudah ce kwance bisa doguwar kujera d'an cikinta yafito, naufal nata aiki, hudah tace AD Allah zan iya ayyukana kabarni yace yarinya wasa kike ba abinda zakiyi, "cikin ikon Allah cikin hudah ya shiga wata takwas, kuma tayi kyau abinta, mammy ne tama naufal waya da yamaido hudah gida amma ya k'iya, saida akayi da gaske kana yamaidata, amma badan yasoba, "saidai kuma shima had'o yanashi yanashi yayi yadawo kt, ranan wata alhamis hudah tatashi da ciwon nak'uda tun tanayi tana d'aukewa haryakai abin yayi yawa, asibiti aka nufa da ita, tun alhamis take nak'uda har washegarin juma'a amma bata haihuba, hankalin kowa yatashi, shiko uban gayyan kuka yake,doctor ne yafito yasamu papa yace yanasan magana dashi, doctor ne yace gaskia saidai amata aiki, tuni papa ya amince yasa hannu dan baibi takan naufal ba,"hudah ce aka turo xa'a kaita theater room, magana tayi tace Amata magana da naufal dayake ta kuka, "zuwa yayi gabanta ya duk'a yana kuka, karka d'amashi kai tayi alamar yadaina kuka, ahankali take magana tace haba AD adua zakaman ba kuka ba plz kadaina kuka kaji? Kad'a Mata kai yayi, tace kuma u make sure kaci abinci inbahakaba zamu b'ata d'agamata Kai yayi murmushi tayi tad'an d'ago tamashi kiss kana aka shiga da ita, awan huda ukku cur kana nurse ta fito tana murmushi, nurse tace toh wazanma congrats cikinku kowa kanta yayo murmushi tayi tace toh ina tayaku Murna hudah tafaifi 3plate wani tsalle naufal yayi kana yafad'i yayi sujada yagodema Allah nanfa akaita murna
Hudah ce a resting room kowa zagaye da ita shiko gogan yakama yara duka ukkun yarik'e saida akayi dagaske kana yabadasu," maza biyu sai mace guda, kuma masu girma Masha Allah, " kwanan hudah ukku asibiti kana aka sallameta dan jikinta yayi kyau, sati ya zagayo yara sukaci sunan abbu da daddynsu fady saikuma macen maaah, amma ana kiran macen iman sai mazan aflan da afnan"daddy kam yaji dad'i maaah kuma harda kukanta, maijego da yara kam sun sami kaya, shima naufal ba'abarshi bayaba dan lefe ya had'ama hudah da babies enta.
Satin hudah ukku da haihuwa kuma Masha Allah yaranta sai firma sukeyi kamar sun kusan shekara,"asatinne akayi bikin fady inda hudah tayi rawan gani itada naufal, ankai amarya gidanta dake hamada carpet , hudah ce zaune tana shirya su aflan naufal yamata waya yace ta shirya gashinan zuwa zasu fita, wanka tayi ta shirya tsaf tana jiran naufal saigashi yazo yaran yatayata d'auka suka fita, basu tsaya ko inaba sai hosptl su maaah tagani da mummy tsaye, mummy sai kuka takeyi, hudah ta tambaya lapia? Shine akacemata Faruq ne bai lapia anma yanke mai k'afa kuma daddy yace baizuwa wajenshi, "d'akin da faruk yake tashiga yana ganinta yafashe da kuka yace hudah kiyafeman hakkinkine ne bina ,"kuka tafashe dashi tace nayafema ya Faruq Allah yabaka lapia,'faruk yace hudah kinemaman gafara wajen maah daddy, girgiza kai hudah tayi tafita tana kuka, tana fita taci Karo da daddy da naufal wajen daddy tatafi da gudu tana kuka tace daddy dan Allah kayafema ya faruk kanta daddy yashafa yace nayafe mashi d'iyata Allah yayimaki albarka kaikuma naufal nagode kwarai dagaske.., hanyarsu ta koma wa gidane take tambayar naufal ya akai yasani,naufal yace maaah ce taman waya tace nakawoki asibiti faruk na asibiti kuma daddy yace baizuwa harsai sanda kikaje idan kinyafemashi, shinefa maaah tace naje nataho da daddy d'in, girgiza kai hudah tayi tana jimamin halin da taga faruk
BAYAN SHEKARA HUDU
Hudah ce zaune tanama iman kalaba suko sojijinta suna wasa, ga d'an karamin cinkinta yafito"naufal ne keta faman gyara hula,"hudah tace wai AD saikuma ina haka, naufal yace Neman aure zani, zumb'uro baki tayi tad'auki pillow gefenta ta jefeshi, dariya yakamayi, ture iman tay, tayi hangar d'akinta da gudu yabita yace haba princess wlhi wasa nake aike kad'aice gidan AD dinki dariya tayi ta rungumoshi, su aflan suma suka dinga dariya, kiransu naufal yayi suna zuwa yahad'asu ya rungume, yace Allah kaine abin godia Allah nagodema dakaban iyalai, dariya hudah tayi ta amin my boss, naufal yace hudah kinzama wani jigo na rayuwana, murmushi hudah tayi tace naufal banda bakin da zansakama saidai ince Allah yak'ara had'a kanmu amin yace yakara kankame iyalanshi.
Meesha na kalla nace nidai Zan aje biro na anan, Meesha tace jirani feedoh nima nan zan tsaya
Godia ta tabbata ga Allah subahanahu wata'alah days bamu ikon gama wanan littafin kurakuran da mukayi Allah kayafemana
Godia ta musamman ga kawata kuma yar uwata lubabatu sani mai tafsir (ilubee) mungode da irin kulawarki akan book ennan
Bamu manta dakuba kawayenmu dakuma yan uwana
Sadiya Marafa
Maryam Ladan Shuni
Feenah s
Mufeen
Rookie sadau
Rookiey kaxs
Safiyya Binji
Zee sifawa
Khady cute
Babylabo
Aysha khalil
Asma'u sambo
Da sauran Wanda bamu fadaba....
Special tnx to nagarta writers association ,mungode da hadinkai da kuka bamu.
Dandalin karatu
Meesha luvs fans
Rookie sadau novels
Muyi zumunci dan Allah
Hausa novel
Zauren karatu
Dasauran groups din dabamu fadaba mungode kwarai.
Wee Lurv u so much our fans❤❤
For any comment or correction here iz my number 08037791855
Tnx so much
www.phirdauceejeebo.mywapblog.com
Written by
Firdausi Abdul'Azeez (Feedoh) &
Ayeesha Musa (Meesha Lurv).
Comments
Post a Comment